5 Disamba 2021 - 16:23
An Fara Kidayar Kuri’u Na Zaben Shugaban Kasar Gambia

A Gambia, ana fara kidayar kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasar da ya gudana a jiya Asabar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA- Zaben shi ne irinsa na farko tun bayan mulkin tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh.

Bayanai daga kasar sun ce zaben ‘yan gudana cikin lumana.

A cen baya dai akan sanar da sakamakon zaben a washe garin kada kuri’ar.

Sama da ‘yan kasar dubu 960 ne aka tantance zasu kada kuria’a a zaben, wanda ake wa kallon zakaren gwajin dafi ga jinjirar demokuradiyyar kasar.

‘Yan takara shida ne suka fafatawa a zaben ciki har da shugaba mai barin gado Adama Barrow da kuma tsohon mataimakinsa Ousainou Darboe, kana madugun ‘yan adawa na kasar.

342/